Gwamnatin Shugaban Kasan Muhammad Buhari Zata Samarwa Matasa Sama Da Milliyon 15 Aikinyi - Duniyarfim.com
  • Breaking News

    Gwamnatin Shugaban Kasan Muhammad Buhari Zata Samarwa Matasa Sama Da Milliyon 15 Aikinyi

    Matasa Milyan 15 Za Su Samu Aikin Yi A
    Gwamnatin Tarayya
    Daga Sheriff Sidi
    Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewar matasa
    milyan 15 za za su samu aikin yi a kokarin da take
    yi na bunkasa tattalin arziki.

    Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaba
    Muhammadu Buhari kan Shirin Bunkasa Tattalin
    Arziki (Economic Recovery Development Plan)
    Malam Sani Yakubu ne ya bayyana hakan a wajen
    bude babban taron Majalisar Koli ta Harkokin
    Kasuwanci, Masana'antu da Saka Jari kashi na tara
    a yau Laraba a otel din Giginya da ke Sakkwato.

    "Babbar manufa ita ce samun nasara a tattalin arziki
    ta hanyar raguwar hauhawar farashi, tsayayyen
    farashin musayar kudi da samar da hanyoyi ga 'yan
    Nijeriya domin su shiga harkokin kasuwanci." Ya
    bayyana.

    Yakubu ya kuma bayyana cewar a karkashin shirin
    al'ummar Nijeriya za su ci gajiya a lamurran
    makamashi da sha'anin wuta da man fetur tare da
    bunkasa sufuri.

    Ya ce ba abin mamaki ba ne yadda Kasuwanci,
    Masana'antu da Saka Jari ya zama daya daga cikin
    fannoni biyar da aka baiwa muhimmanci domin fita
    daga matsin tavarvarewar tattalin arziki a Nijeriya.

    A jawabinsa Babban Sakataren Ma'aikatar
    Kasuwanci, Masana'antu da Saka Jari ta Kasa, Mista
    Edet Sunday Akpan ya bayyana cewar a baya-bayan
    nan Tattalin Arzikin Nijeriya ya fuskanci kalubale
    sosai musamman ta dalilin tabarbarewar Tattalin
    Arzikin Duniya bakidaya a bisa ga dogara kacokam
    kan man fetur.

    Akpan ya bayyana cewar a yanzu haka Nijeriya ta
    fita daga kangin tabarbarewar tattalin arziki da kashi
    0.55% wanda kuma yake karuwa.

    No comments