Anbude Sabon Gidan Cin Abinci Tsirara A Kasar Faransa
Subuhanallahi.
Innalillahi wainna ilaihi raji'un.
Alumma Wannan duniyar fa tazo karshe.
A Faransa An Bude Sabon Gidan Abinci Da
Mutane Zasu Dinga Zuwa Zigidir
A kasar Faransa an bude wani sabon gidan
abinci da mutane zasu dinga zuwa cin abinci
zigidir.
Sabon gidan abinci mai suna O’naturel
an bude shi ne a babban birnin kasar Faris,
sabon gidan abincin zai baiwa dangi da iyalai
damar zuwa su yi karin kumallo ko cin abincin
rana ko cin abin dare.
An dai bude wannan sabon gidan abincin ne a
ranar Juma’ar nan da ta gabata, bayan da masu
rajin yawo tsirara sukai ta kiraye kirayen a bude
shi, domin suje su gwangwaje tare da iyalansu.
Manajan gidan sabon abincin Mista Stephane
Saada, ya bayyana jin dadin kan irin yadda
jama’a ke tururwa zigidir suna zuwa domin su ci
abinci a wajensu.
Yace wannan abin da mutane
ke yi ya kara musu kwarin guiwa, kuma zasu
zage dantse wajen ganin sun hidimtawa
mutane.
Haka nan, suma masu makwabtaka da gidan
abincin sun nuna jin dadinsu kan yadda aka
bude sabon gidan abincin da zai basu damar
zuwa cin abinci da iyalansu zigidir.
A wannan gidan abinci, kudin abinci mafi arha
shine wanda kudinsa ya kama kudin tarayyar
turai (Euro 30) Kimanin Naira 12,420. Jama’a
da dama sun bayyana farashin da cewar bai yi
tsada ba.
Allah daya gari bamban.
ALLAH KASA MU CIKA DA KALMAR (LÃILAHA
ILLALLAHU MUHAMMAD RASULILLAHI).

No comments