Jarumin Kannywood Ya Zama Jakadan Majalisar Dinkin Duniya - Duniyarfim.com
  • Breaking News

    Jarumin Kannywood Ya Zama Jakadan Majalisar Dinkin Duniya



    Fittaccen dan wassan kwaikwayo kuma mawaki
    Sani Danja ya samun sabon mukami a majalisar
    dinkin duniya inda aka nada shi a matsayin
    jakada a fannin kafa manufa ta samun cigaban
    zamani (SDGs) ta majalisar.

    Anyi taron kaddamar da jarumai a garin Abuja
    ranar laraba 25 ga watan octoba yayin da ake bikin
    nuna farin ciki zagoyowar ranar majalisar dinkin
    duniya.
    Danja wanda aka fi sani da 'sarkin nishadi na
    arewa' ya shahara a fadin Nijeriya bisa ga rawan
    da yake taka wa a harkar nishadantarwa.

    Wannan sabon daukaka yana cikin jerin jakadanci
    da ya samu daga kamfanin Glo, Rotary, gidauniyar
    save the children, western loto da sauran su.

    Banda Sani Danja sauran jaruman kannywood da
    suka samu mukamin jakadanci na majalisar dinkin
    duniya akwai Yakubu Muhammed da Uzee Usman.


    A cikin manyan baki da suka halarci taron akwai
    Ministan wassannin da ayyukan matasa Solomon
    Dalung da babban mataimakin shugaban kasa a
    kan SDGs Princess Adejoke Orelope Ade Fulure.


    Sauran jaruman Nijeriya da suka samu matsayin
    sun hada da mawaki Tuface, Sunny Ade, Omotola
    jalade Ekehinde, Chigurl, Teju babyface, Alibaba
    da Zdon Paporella .

    No comments