Shugaban Kasa Muhammad Buhari Yayima Jama,ar Nigeria Barka Da Sallah
SAKON GORON SALLAR SHUGABA BUHARI GA 'YAN
NAJERIYA.
Ya 'Yan Uwana 'Yan Najeria
Ina mai matukar taya ku murna dukkanin ku,
musamman ma Musulmai daga cikinku na wannan
ranar Sallar Idi babba (Eid-El-Kabir) na wannan
shekarar.
Haka kuma ina taya 'Yan uwa musulmanmu maza
da mata da suke kasa mai tsarki (Makka) a yanzu
haka domin gudanar da aikin Hajjin wannan
shekarar.
Amma daga farko ina so zan yi amfani da wannan
damar domin in yi muku godiya bisa irin addu'oin
da ku ka yi ta gudanarwa a kaina domin samun
lafiyata da kuma fatar alheri da kuma murna
dawowa ta Nijeriya.
Hakika addu'oinku da kuka dukufa kukaita
gudanarwa akaina wacce da hanada musulmanku
da kiristoci daga cikinku dama masu mabanbantan
ra'ayin siyasa dama kabilu daban-daban daga
cikinku, hakika sun kara mun kwarin guiwa da kara
dagewata sosai dama gwaunatinmu domin gina
wannan kasa tamu ta cigaba.
Daga bangaren shagalin bikin sallar layyar wannan
shekarar, ina rokon dukkanin 'Yan Najeriya da mu
aje banbance-banbancen dake tsakaninmu, mu
watsar da tsana da tsangwama mu rungumi
zumunci da abota da 'Yan uwantaka da kuma hadin
kai domin mu ciyarda kasarmu Najeriya gaba
Daga bangaren musulmi na duniya kuma, manufar
wannan bikin shine tuna irin jarabawar da ubangiji
yayiwa annabi Ibrahim na yanka dansa ne da kuma
irin mika wuyar da yayi wurin biyayya ga umarnin
mahaliccinsa ne.
Kamar yadda muke cike da farin cikin wannan bikin,
inada yakinin wannan kasa tamu zata samu cigaba
cikin sauri ta kowani bangare idan mukayi koyi da
halayen annabi Ibrahim ta hanyar sadaukar da kai,
hakuri, son juna, kwazo da kuma biyayya ga
umarnin ubangijinmu da kuma kiyaye dokokin
hukuma
Dole ne mu koyawa kanmu son juna da kuma
daukar kanmu a matsayin 'Yan uwa maza da mata
wadanda mukeda tarihi iri daya kuma dole ne mu
zama kamar yadda wata karin magana ta 'Yan Afrika
take cewa "Iyalai kamar bishiya ce, za ta iya
lankwashewa amma ba za ta karye ba"
Haka kuma har wayau dai, ina mai tabbatar muku
cewar wannan gwaunatin wacce ta dauki harkar
tsaron kasa, tattalin arziki da walwalar yan kasa a
matsayin ababe masu muhimmanci data sanya a
gaba, ba zata taba gajiyawa ba har saita cimma
gurinta na samarda sabuwar Najeriya mai cike da
zaman lafiya tattalin arziki mai yalwa da kuma
cigaban jama'a.
Ina yi wa kowa da kowa barka da sallah kuma a yi
biki lafiya.
MUHAMMADU BUHARI
31/AGUSTA/2017.
NAJERIYA.
Ya 'Yan Uwana 'Yan Najeria
Ina mai matukar taya ku murna dukkanin ku,
musamman ma Musulmai daga cikinku na wannan
ranar Sallar Idi babba (Eid-El-Kabir) na wannan
shekarar.
Haka kuma ina taya 'Yan uwa musulmanmu maza
da mata da suke kasa mai tsarki (Makka) a yanzu
haka domin gudanar da aikin Hajjin wannan
shekarar.
Amma daga farko ina so zan yi amfani da wannan
damar domin in yi muku godiya bisa irin addu'oin
da ku ka yi ta gudanarwa a kaina domin samun
lafiyata da kuma fatar alheri da kuma murna
dawowa ta Nijeriya.
Hakika addu'oinku da kuka dukufa kukaita
gudanarwa akaina wacce da hanada musulmanku
da kiristoci daga cikinku dama masu mabanbantan
ra'ayin siyasa dama kabilu daban-daban daga
cikinku, hakika sun kara mun kwarin guiwa da kara
dagewata sosai dama gwaunatinmu domin gina
wannan kasa tamu ta cigaba.
Daga bangaren shagalin bikin sallar layyar wannan
shekarar, ina rokon dukkanin 'Yan Najeriya da mu
aje banbance-banbancen dake tsakaninmu, mu
watsar da tsana da tsangwama mu rungumi
zumunci da abota da 'Yan uwantaka da kuma hadin
kai domin mu ciyarda kasarmu Najeriya gaba
Daga bangaren musulmi na duniya kuma, manufar
wannan bikin shine tuna irin jarabawar da ubangiji
yayiwa annabi Ibrahim na yanka dansa ne da kuma
irin mika wuyar da yayi wurin biyayya ga umarnin
mahaliccinsa ne.
Kamar yadda muke cike da farin cikin wannan bikin,
inada yakinin wannan kasa tamu zata samu cigaba
cikin sauri ta kowani bangare idan mukayi koyi da
halayen annabi Ibrahim ta hanyar sadaukar da kai,
hakuri, son juna, kwazo da kuma biyayya ga
umarnin ubangijinmu da kuma kiyaye dokokin
hukuma
Dole ne mu koyawa kanmu son juna da kuma
daukar kanmu a matsayin 'Yan uwa maza da mata
wadanda mukeda tarihi iri daya kuma dole ne mu
zama kamar yadda wata karin magana ta 'Yan Afrika
take cewa "Iyalai kamar bishiya ce, za ta iya
lankwashewa amma ba za ta karye ba"
Haka kuma har wayau dai, ina mai tabbatar muku
cewar wannan gwaunatin wacce ta dauki harkar
tsaron kasa, tattalin arziki da walwalar yan kasa a
matsayin ababe masu muhimmanci data sanya a
gaba, ba zata taba gajiyawa ba har saita cimma
gurinta na samarda sabuwar Najeriya mai cike da
zaman lafiya tattalin arziki mai yalwa da kuma
cigaban jama'a.
Ina yi wa kowa da kowa barka da sallah kuma a yi
biki lafiya.
MUHAMMADU BUHARI
31/AGUSTA/2017.

No comments