Dalilin Da Yasa Nake Qalu Balantar Malam Nasiru El'rufa,i Tijjani Ramadan
Dalilin Da Ya Sa Nake Kalubalantar Gwamna El-
Rufa’i, Inji Tijjani Ramalan
Alhaji Tijjani Ramalan, gogaggen dan siyasa ne, har
ila yau kuma Shugaban Kungiyar Masu Fafutukar
Dawo Da Martabar Jihar Kaduna (Kaduna
Restoration Group) a turance.
A tattaunawarsa da
Manema labarai a kaduna, ya yi fashin baki kan
harkokin siyasay Kaduna da na Nijeriya baki daya.
Ga yadda ta kasance.
Ku ne kan gaba a lokacin yakin neman zaben
Gwamna el-Rufai, yanzu kuma kun raba gari, shin
me yake faruwa ne?
Ina son na yi bayani a nan na kuma warware komai
daki-daki, mu ba wai muna maida hanun agogo
baya bane, ko kuma muna kokarin taka wa el-Rufa’I
burki bane.
Mambobin kungiyarmu da yawansu
daga jami’iyyar APC suke, a yayin da wasu
mambobin suka fito daga sauran jam’iyyun kasar
nan, inda suka taimaka sosai wajen kawo wannan
gwamnatin daga matakin jiha da kasa baki daya ta
fuskoki da daman gaske kuwa.
Babban manufarmu dai ita ce mu tabbatar da
kyakyawan shugabanci.
Don haka, mu bamu neman
kawo wa Malam Nasiru el-Rufa’I cikas.
Amma mun
sani gwamnati dai ya ci rabin zango daga cikin
shekarunta hudu da ke gabata, akwai bukatar mu
bawa gwamna shawarori masu muhimmanci domin
a samu nasara tafiyar da lamura yadda suka dace.
Wannan dalilin ne ya sanya muka hada kanmu
domin fitar da takardar manema labaru. Mun rubuta
wasiku da dama zuwa ga gwamnan. Za kuma mu ci
gaba da hakan, za mu kasance abokan gwamnan ta
hanyar alkalaminmu.
Domin muna son a samu
shugabanci mai kyau kuma mai inganci a jihar
Kaduna, don haka ne muke fadi tashin saita komai
bisa daidai. Yanzu zan kasance abokin gwamnati ta
hanyar ALKAMI.
Me ya sa ka zabi zama abokin gwamna ta wannan
hanyar maimakon tukararsa ka tsaye?
Na kasance shugaban APC a Kaduna, na sani da
yawan mambobin da suke tutiya da APC sun yi
kaura ne daga jam’iyyun da suka hada da CPC.
Na shiga jam’iyyar CPC ne bayan da na bar PDP, bayan
da na iya fahimci PDP tana durkushewa.
Da dama
mutane sun shiga APC ne daga jam’iyyar PDP kai
har da shi kansa el-Rufa’i.
Maganar gaskiya ita ce dukkaninmu kowa ya yi
kokari wajen tilastawa amsar karfin mulki daga
hanun PDP daga matakin jihohi, kuma ba abun
mamaki bane hakan.
Na sadaukar da komai domin
tabbatar da cewar mun kawar da PDP a jihar
Kaduna.
Domin da daman mu mun so hakan kuma
mun yi nasarar fatattakar PDP a jihar nan.
Na yi hidima sosai a APC, na kuma yi yaki sosai;
na kuma rungumi kasada sosai.
Ba zan taba
mancewa ba; akwai gwamnan Kaduna da tsohon
mataimakin shugaban kasa Namadi Sambo wanda
shi ma daga jihar Kaduna yake.
Gaskiya na fuskanci
kalubale da yawa.
A takaice ma hatta gidan
rediyona na Liberty ya gamu da suka kan cewar ina
yi wa APC kamfe.
Kuma har yau din ban yi nadamar
tallata jami’iyyar da na yi ba, da kuma gagarumar
gudunmawar da na bayar wajen yada manufar APC
da kuma kawar da PDP.
Babu wata dokar Nijeriya da ta haramta dukkanin
gidan jarida ko gidan rediyo kada kuri’a ga
jami’iyyun siyasa.
Wannan dalilin ne ya sanya
Liberty Radio da TB suka tsaya gami da bin bayan
shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari da Nasir el-
Rufa’i.
Gaskiyar magana mun tari aradu da ka.
Da PDP ta
yi nasara a zaben da aka fafata, Allah ne kadai ya
san mene ne zai iya faruwa da mutane irina da suka
yi tsayuwar daka don kawar da ita.
Kowa ya san da
wannan, na yi imanin da PDP ta yi nasara da ni kam
sai na fuskacin barazana sosai, domin na yi hidima
fiye da kima don kawo APC.
Mun yi tsammanin
Nasiru el-Rufa’i zai yi amfani da ikonsa wajen
daukaka darajar jiharmu gami da kaita babban
mataki, amma kuma sai muka ga yana sauka daga
kan tsari, yana biye wa masu dora shi a keken bera.
Yau shekara biyu da hawan wannan gwamnati, shin
ra’ayinka a kanta ya canja ne?
Shekaru biyu sun gabata a mulkinsa, muna kokarin
ba shi shawarori ga-mu-ga-ga-shi, akwai wandanda
muka rigaya muka yi masa, ta hanyoyin rubuta
takarda da sauransu.
A matsayina na shugaban kungiyar da ke fafatukar
farfado da jihar Kaduna, ina da alaka ta kai tsaye
da gwamna.
Ba sau daya ba, ba kuma sau biyu ba,
na sha jawo hankalin gwamnan Kaduna dangane da
nade-naden mukamai, na ke ce masa ba fa zai
tsaya yin amfani da zallar ‘yan APC bane, dole ne
ya duba sauran jam’iyyun domin akwai wadanda
suka yi masa hidima har ya zama gwamna.
Na bashi shawara kada ya kuskura ya tsuke hannunsa
wajen zallar APC ya yi kokari ya surka da sautan
mutunen jam’iyyun siyasan.
Domin ina da ilimin
siyasa jiya da yau, na kuma san abubuwan da suka
dace a siyasance.
Na kasance dan siyasa yau sama da shekaru 30,
akalla ina da ilimi kuma na dauki darussa sosai
daga wasu.
Na fara harkar siyasa ne tun a 1983 a
karkashin jam’iyyar (NPN).
Na taba zama wakili na
musamman ga gwamnan jihar Ribas marigayi Chief
Melford Okilo a jihohin Arewa.
Wanda ofishina ke
jihar Kaduna.
Bayan nan kuma, na zo na kasance
shugaban (NRC), kafin hakan na zama mamba a
kwamitin (NRC) da dai sauransu.
Source By Rariya
Rufa’i, Inji Tijjani Ramalan
Alhaji Tijjani Ramalan, gogaggen dan siyasa ne, har
ila yau kuma Shugaban Kungiyar Masu Fafutukar
Dawo Da Martabar Jihar Kaduna (Kaduna
Restoration Group) a turance.
A tattaunawarsa da
Manema labarai a kaduna, ya yi fashin baki kan
harkokin siyasay Kaduna da na Nijeriya baki daya.
Ga yadda ta kasance.
Ku ne kan gaba a lokacin yakin neman zaben
Gwamna el-Rufai, yanzu kuma kun raba gari, shin
me yake faruwa ne?
Ina son na yi bayani a nan na kuma warware komai
daki-daki, mu ba wai muna maida hanun agogo
baya bane, ko kuma muna kokarin taka wa el-Rufa’I
burki bane.
Mambobin kungiyarmu da yawansu
daga jami’iyyar APC suke, a yayin da wasu
mambobin suka fito daga sauran jam’iyyun kasar
nan, inda suka taimaka sosai wajen kawo wannan
gwamnatin daga matakin jiha da kasa baki daya ta
fuskoki da daman gaske kuwa.
Babban manufarmu dai ita ce mu tabbatar da
kyakyawan shugabanci.
Don haka, mu bamu neman
kawo wa Malam Nasiru el-Rufa’I cikas.
Amma mun
sani gwamnati dai ya ci rabin zango daga cikin
shekarunta hudu da ke gabata, akwai bukatar mu
bawa gwamna shawarori masu muhimmanci domin
a samu nasara tafiyar da lamura yadda suka dace.
Wannan dalilin ne ya sanya muka hada kanmu
domin fitar da takardar manema labaru. Mun rubuta
wasiku da dama zuwa ga gwamnan. Za kuma mu ci
gaba da hakan, za mu kasance abokan gwamnan ta
hanyar alkalaminmu.
Domin muna son a samu
shugabanci mai kyau kuma mai inganci a jihar
Kaduna, don haka ne muke fadi tashin saita komai
bisa daidai. Yanzu zan kasance abokin gwamnati ta
hanyar ALKAMI.
Me ya sa ka zabi zama abokin gwamna ta wannan
hanyar maimakon tukararsa ka tsaye?
Na kasance shugaban APC a Kaduna, na sani da
yawan mambobin da suke tutiya da APC sun yi
kaura ne daga jam’iyyun da suka hada da CPC.
Na shiga jam’iyyar CPC ne bayan da na bar PDP, bayan
da na iya fahimci PDP tana durkushewa.
Da dama
mutane sun shiga APC ne daga jam’iyyar PDP kai
har da shi kansa el-Rufa’i.
Maganar gaskiya ita ce dukkaninmu kowa ya yi
kokari wajen tilastawa amsar karfin mulki daga
hanun PDP daga matakin jihohi, kuma ba abun
mamaki bane hakan.
Na sadaukar da komai domin
tabbatar da cewar mun kawar da PDP a jihar
Kaduna.
Domin da daman mu mun so hakan kuma
mun yi nasarar fatattakar PDP a jihar nan.
Na yi hidima sosai a APC, na kuma yi yaki sosai;
na kuma rungumi kasada sosai.
Ba zan taba
mancewa ba; akwai gwamnan Kaduna da tsohon
mataimakin shugaban kasa Namadi Sambo wanda
shi ma daga jihar Kaduna yake.
Gaskiya na fuskanci
kalubale da yawa.
A takaice ma hatta gidan
rediyona na Liberty ya gamu da suka kan cewar ina
yi wa APC kamfe.
Kuma har yau din ban yi nadamar
tallata jami’iyyar da na yi ba, da kuma gagarumar
gudunmawar da na bayar wajen yada manufar APC
da kuma kawar da PDP.
Babu wata dokar Nijeriya da ta haramta dukkanin
gidan jarida ko gidan rediyo kada kuri’a ga
jami’iyyun siyasa.
Wannan dalilin ne ya sanya
Liberty Radio da TB suka tsaya gami da bin bayan
shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari da Nasir el-
Rufa’i.
Gaskiyar magana mun tari aradu da ka.
Da PDP ta
yi nasara a zaben da aka fafata, Allah ne kadai ya
san mene ne zai iya faruwa da mutane irina da suka
yi tsayuwar daka don kawar da ita.
Kowa ya san da
wannan, na yi imanin da PDP ta yi nasara da ni kam
sai na fuskacin barazana sosai, domin na yi hidima
fiye da kima don kawo APC.
Mun yi tsammanin
Nasiru el-Rufa’i zai yi amfani da ikonsa wajen
daukaka darajar jiharmu gami da kaita babban
mataki, amma kuma sai muka ga yana sauka daga
kan tsari, yana biye wa masu dora shi a keken bera.
Yau shekara biyu da hawan wannan gwamnati, shin
ra’ayinka a kanta ya canja ne?
Shekaru biyu sun gabata a mulkinsa, muna kokarin
ba shi shawarori ga-mu-ga-ga-shi, akwai wandanda
muka rigaya muka yi masa, ta hanyoyin rubuta
takarda da sauransu.
A matsayina na shugaban kungiyar da ke fafatukar
farfado da jihar Kaduna, ina da alaka ta kai tsaye
da gwamna.
Ba sau daya ba, ba kuma sau biyu ba,
na sha jawo hankalin gwamnan Kaduna dangane da
nade-naden mukamai, na ke ce masa ba fa zai
tsaya yin amfani da zallar ‘yan APC bane, dole ne
ya duba sauran jam’iyyun domin akwai wadanda
suka yi masa hidima har ya zama gwamna.
Na bashi shawara kada ya kuskura ya tsuke hannunsa
wajen zallar APC ya yi kokari ya surka da sautan
mutunen jam’iyyun siyasan.
Domin ina da ilimin
siyasa jiya da yau, na kuma san abubuwan da suka
dace a siyasance.
Na kasance dan siyasa yau sama da shekaru 30,
akalla ina da ilimi kuma na dauki darussa sosai
daga wasu.
Na fara harkar siyasa ne tun a 1983 a
karkashin jam’iyyar (NPN).
Na taba zama wakili na
musamman ga gwamnan jihar Ribas marigayi Chief
Melford Okilo a jihohin Arewa.
Wanda ofishina ke
jihar Kaduna.
Bayan nan kuma, na zo na kasance
shugaban (NRC), kafin hakan na zama mamba a
kwamitin (NRC) da dai sauransu.
Source By Rariya

No comments