Hadiza Gabon Ta Maidawa Da Wani Matashi Martani - Duniyarfim.com
  • Breaking News

    Hadiza Gabon Ta Maidawa Da Wani Matashi Martani


    Ko Za Ka Baiwa Tsoho Shawara Ya Yi Wa Tsohuwa
    Ritaya Ya Auro Ni?, Martanin Hadiza Gabon Ga
    Wani Matashi Da Ya Nemi Ta Yi Aure
    Jarumar Finafinafin Hausa Hadiza Aliyu Gabon, Ta
    Mayarwa Wani Matashi Martani A Shafinta Na
    Twitter.

    Shidai Matashin Mai Suna M. Bash Ya ba ta
    Shawarar Cewa, Ta fidda Miji Ta yi Aure Tunda Ta
    Girma, A Daidai Lokacin Da Ta Sanya Wani Hotonta
    A Shafin nata Na Twitter.

    Furucin Matashin Bai yi wa Hadiza Gabon Dadi ba,
    Inda Ta Mayar mishi Da Raddin Cewa, Ya je Ya
    kaiwa Mahaifinsa Shawarar Ya yi wa Mahaifiyar shi
    Ritaya, In Ya so Sai Ya Maye Gurbin Mahaifiyarta
    shi Da Ita.

    Mun yi Kokarin Jin Ta bakin Hadiza Gabon Don Jin
    Komai Ya Harzuka ta Har tayi Wannan Raddin, Duk
    Da Al'umma Suna Mata Kallo Mai Hakuri Kuma
    Wacce Ta Shahara Wajen Tallafawa Al'umma Masu
    Karamin Karfi, Sai Dai Hakar mu Bata Cimma Ruwa
    ba, Domin Mun yi Ta Kiran Lambarta Amma A Rufe,
    Kuma Mun Aike mata Da Sakon Shi ma Har yanzu
    Bai shiga ba.

    Duk Wanda Yak eso Ya ga Wannan Raddin Na
    Hadiza Aliyu Gabon Sai Ya Ziyarci Shafinta Na
    Twitter.

    No comments